Yan Bindiga Sun Harbe Mutane Biyu Tare Da Sace Ɗan Kasuwa A Kano

Yan bindiga a ranar Litinin sun yi garkuwa da wani ɗan kasuwa, Nasiru Na’ayya dake kauyen Gangarbi dake karamar hukumar Roggo ta jihar Kano.

Wani shedar gani da ido wanda dan uwa ne ga mutumin ya ce yan bindigar sun farma ƙauyen da misalin ƙarfe 12:00 na dare inda suka fara harbin iska.

“Lokacin da mutanen yankin suka yi yunkurin hana yan bindigar tafiya da mutumin sun harb mutane biyu wanda ya jawo mutuwar mutum guda nan take guda kuma ya jikkata inda yanzu haka yake samun kulawa a asibiti.”

A cewar wani da ya nemi a sakaye sunansa ya ce Gangarbi da makotan ƙauyuka da suka haɗa da Bari da Gwangwan a yan kwanakin nan sun fuskanci hare-hare daga yan bindiga.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce kawo yanzu bashi da masaniya kan harin.

More News

Jihar Neja za ta riƙa biyan  ₦80,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago ya amince a riƙa biyan ₦80,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan jihar. Gwamnan ya amince da fara biyan...

Jam’iyar NNPP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin jihar Kano

Jam'iyar New Nigeria People Party NNPP ta lashe zaɓen  dukkanin kujerun ƙananan hukumomin jihar Kano 44. Farfesa Sani Malumfashi shugaban hukumar zabe mai zaman kanta...

Jam’iyar NNPP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin jihar Kano

Jam'iyar New Nigeria People Party NNPP ta lashe zaɓen  dukkanin kujerun ƙananan hukumomin jihar Kano 44. Farfesa Sani Malumfashi shugaban hukumar zabe mai zaman kanta...

Wani sojan ruwan Najeriya ya hallaka abokin aikinsa a Zamfara

Hedikwatar Tsaron Najeriya ta kama wani sojan ruwa mai suna A. Akila bisa zarginsa da kashe abokin aikinsa.An tura Akila zuwa sansanin Forward Operating...