Yan bindiga sun buɗe wuta kan daraktan yakin neman zaben Atiku a Rivers

Wasu yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun buɗe wuta akan ayarin motocin, Dr.Abiye Sekibo4 darakta janar na yakin neman zaben Atiku Abubakar a jihar Rivers.

Yan bindigar dake sanye da kakakin yan sanda sun buɗe wuta akan ayarin motocin a Rainbow Town dake birnin Fatakwal.

Sekibo yaje ziyarar duba wurin da za a gudanar da taron yaƙin neman zaben shugaban kasa na jam’iyar PDP a jihar.

A yayin kai harin Sekibo na cikin motar sulke kawo yanzu rundunar yan sandan jihar bata fitar da waya sanarwa ba kan faruwar lamarin.

More from this stream

Recomended