‘Yan Banga Da Mafarauta Sun Sami Horon Cudanya Da Al’umma

A ci gaba da neman mafita ga matsalar tsaro a Nijeriya, Majalisar dinkin duniya, karkashin shirin taimakawa kasashe masu tasowa, ta horadda ‘yan kato da gora, ‘yan banga da mafarauta.

Majalisar ta koyar da su dabarun cudanya da al’umma da hada kai da jami’an tsaro, don samun mafita kan matsalar tsaro a Arewa maso gabashin Najeriya.

Matasa dari hudu ne daga jihohin Adamawa da Yobe, suka zo cibiyar koyar da dabarun shugabanci da zama dan kasa na gari a Jos jihar Filato.

An horar da su yadda zasu kaucewa take hakkin dan adam, fahimtar darajar al’adun al’umma da hadin kai wajen gudanar da aikinsu ba tare da nuna bambancin addini ko kabila ba.

More News

DA ƊUMI-ƊUMI: DSS sun cafke Sowore a filin jirgin na Legas

Jami'an Hukumar Ƴansandan Farin-kaya ta DSS sun kama Omoyele Sowore, jagoran kungiyar  #RevolutionNow Movement da ke adawa da gwamnati a filin jirgin sama na...

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...