Wata mata mai juna biyu mai suna Hauwa Isah ta rasa ranta a hannun mijinta, Mohammed Sani, wanda ake zargin ya yi mata duka har lahira a unguwar Limawa da ke birnin Minna, jihar Neja.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 10:30 na dare a ranar Talata, inda mazauna unguwar suka ce sun ji ihun Hauwa daga gidansu kafin daga bisani su same ta kwance cikin jini.
Wata makwabciya mai suna Halima Musa ta ce kafin a kai dauki, Hauwa ta riga ta mutu. Ta kara da cewa wannan ba shi ne karon farko da mijin ke dukan matarsa ba.
Mahaifin mamaciyar, cikin kunci da alhini, ya bayyana cewa an sha jan kunnen Mohammed kan cin zarafin matarsa amma bai daina ba. “Mun gargade shi sau da dama, amma bai saurara ba. Yanzu ya kashe ta,” in ji mahaifin.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an kama wanda ake zargi da laifin kisan kai. A cewarsa:
“A ranar 3 ga Yuni, 2025, da misalin karfe 10:30 na dare, an samu kiran gaggawa daga wani gida da ke unguwar Bani Hashimu Estate, Limawa ‘A’ Minna cewa an sami wata mace mai suna Hauwa Isah mai shekaru 24 a kasa cikin jini.”
SP Abiodun ya ce jami’an ‘yan sanda daga ofishin A Division Minna sun garzaya zuwa wurin da lamarin ya faru, inda suka samu gawar Hauwa a kasa cikin dakin. An garzaya da ita asibitin Minna, inda aka tabbatar da mutuwarta. Haka kuma, likitoci sun tabbatar da cewa tana da juna biyu na wata tara kafin rasuwarta.
Mohammed Sani, wanda ke da shekaru 31, yanzu haka yana hannun ‘yan sanda, kuma ana shirin mika shi zuwa sashin binciken manyan laifuka (SCID) a Minna don ci gaba da bincike.
Al’ummar yankin da wannan mummunan lamari ya faru na bukatar hukunci mai tsauri da kuma daukar matakai don kare mata daga cin zarafi a cikin aure.