Yadda wani ango ya kashe tare da banka wa amaryarsa wuta har lahira

Ana zargin wani mai suna Motunrayo Olaniyi ya daba wa sabuwar amaryar sa, Olajumoke wuka har lahira, bayan wata zazzafar muhawara a gidan Amazing Grace Estate da ke Elepe a yankin Ikorodu a jihar Legas.  

An ce Olaniyi mai shekaru 30 da haihuwa ya daba wa matarsa mai shekaru 25 wuka sau da dama, inda ya kulle ta a dakin sannan ya banka mata wuta.

Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, 4 ga watan Oktoba, 2024, bayan da ma’auratan suka samu sabani.

A cewar Benjamin Hundeyin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Legas, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar. 

Ya bayyana cewa wanda ake zargin ya kuma raunata kansa bayan ya aikata laifin.

Sai dai tawagar ‘yan sandan da suka isa wurin an ce sun kashe gobarar inda daga bisani suka gano gawar Olajumoke da raunuka a cikinta.

More News

TCN na ci gaba da ƙoƙarin gyaran wutar lantarkin da ta lalace kwana biyu

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya sanar da ci gaban da aka samu wajen farfado da rukunin wutar kasa bayan wata tangardar...

Magoya bayan jam’iyyar NNPP sun Æ™ona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

PDP ta É—auki hanyar warware rikicin jam’iyyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami'yar PDP. Mohammed wanda shi ne shugaban Æ™ungiyar gwamnonin...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu Æ´an’aiken Æ´anbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...