Yadda rikicin kabilanci ya janyo takaddama a Taraba | BBC Hausa

Wasu al’ummomin Hausawa da Fulani da kuma barebari ‘yan asalin garin Wukari da ke jihar Taraba da ke arewa maso gabashin Najeriya sun zargi hukumomi da hana su komawa mazauninsu tun bayan rikicin da aka yi mai nasaba da kabilanci da kuma addini shekara 7 da ta gabata, abin da ya tilasta masu zaman gudun hijira a wasu yankunan jihar.

Mutanen na unguwar Sabon Gari, sun ce kimanin shekara 5 ke nan da ta gabata suke kokarin komawa gidajensu amma abin ya ci tura.

Rikicin na shekara ta 2013 dai ya yi sanadiyyar rasa dimbin rayuka da dukiyoyi a garin na Wukari. Jihar Taraba dai na daga cikin jihohin da ke fama da rikice-rikce tsakanin kabilu, musamman Jikunawa da Tibabe da kuma kabilun da ke da nasaba da Hausawa.

Abdu Ali, daya daga cikin mazauna yankin na Sabon gari ya ce suna gudun hijra a wasu wuraren kuma bayan shekarun da suka yi ba a gidajensu bane suka fara kokarin komawa mazauninsu.

Ya ce “wasu daga cikinmu har sun yunkura ma sun fara kai kayan aiki suna fara gini toh sai a turo (matasa) sai su zo su rusa mana wadannan gidaje da muke ginawa. Suyn riga sun kona wurin ya koma fili,”

“Muna zargin Sarkin Wukari da (shugaban) karamar hukumar ta Wukari su suke tura su suke rushe mana gidaje. Mun yi iya bakin kokarinmu mun (zabi) wasu mutane daga cikinmu aka tura sai aka ce ai Sarkin yana fushi da wasu mutane mazauna sabon garin Wukari.” in ji Abdu Ali.

Amma Danladi Baushe, wanda shi ne Madakin Uka Wukari ya karyata zargin al’ummar na Sabon Garin inda ya ce “mun sanar da kowa cewa duk wanda zai zo ya tabbatar ya zauna dai-dai wurinsa kada ya yadda ya shiga gidan wani ko taku daya gidan makocinsa,”

Game da zargin da al’ummar suka yi na cewa Sarkin na Wukari ya ki amincewa mutanen su dawo gidajensu ba, Baushe ya ce “karya ne ana so a bata masa suna ne.”

Ya kuma ce akwai wadanda suka dawo amma wasu na kokarin dawowa kafin karshen shekarar nan.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

ÆŠan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...