Yadda Rikicin Boko Haram Ya Shafi Harkokin Kasuwanci

A Najeriya, sama da shekaru goma kenan, da dakarun kasar suke ta fafatawa da mayakan kungiyar Boko Haram mai ta da kayar baya, musamman a arewa maso gabashin kasar.

Jihar dai da ta fi fuskantar hare-haren kungiyar, ita ce ta Borno, lamarin da ya yi mummunan tasiri akan tattalin arzikin yankin.

Wannan tasiri na koma-baya da aka gani musamman a ‘yan shekarun da suka gabata, ya jefa al’umar yankin musamman ‘yan kasuwa cikin halin ni-‘yasu.

Bincike ya nuna cewa, fannini da dama na harkokin kasuwanci a jihar ta Borno, sun fuskani koma baya matuka.

Koda yake, ba a kare a wuri guda ba, domin yayin da wasu bangarorin kasuwanci suka farfado, wasu kuwa har yanzu akwai sauran jan aiki a gaba.

Gwoza, ita ce karamar hukumar farko da ‘ya’yan kungiyar ta Boko Haram suka taba kwacewa, an kuma taba rufe babbar kasuwa garin, sanadiyyar hare-haren kungiyar, ko da yake, al’amura sun daidaita domin tuntuni aka bude kasuwar

“A gaskiya lokacin da aka rufe kasuwar nan mutane sun shiga damuwa, a lokacin da jarrabawa na Boko Haram ya same mu, an rufe kasuwar nan saboda kada su samu dama su zo su abkawa mutane.” Inji tsohon shugaban karamar hukumar ta Gwoza, Alhaji Abdullahi.

Ya kara da cewa, “amma da ikon Allah da sojoji suka tsaya tukuru, mutanenmu sun koma gida, kasuwan nan bude ta, a Gaskiya yanzu kasuwr tana cika makil.”

Sai dai ba kamar ‘yan kasuwar ta Gwoza ba, fannin sarrafa burodi ya shafu matuka, kuma har yanzu a cewar shugabansu, Malam Bukar Mustapha, harkar gasa burodi, ba ta dawo yadda take ba.

“Kafin zuwan wannan matsalar tsaro, muna da gidajen burodi da suka kai 500… amma yanzu ba su fi 150 ba.” Inji Mustapha.

Ya kara da cewa, hare-haren da aka kai a yankunan “Bama, Gamboru Ngala, Gwoza, Damboa, Monguno da Damasak,” har yanzu babu wanda ya samu karfin tasowa.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...