Yadda PDP, ZLP Suka Kalubalanci Gwamna Akeredolu Na APC a Zaben Ondo

Zaben na ranar Asabar na zuwa ne kasa da wata guda bayan wanda aka yi a jihar Edo a kudu maso kudancin Najeriyar, wanda PDP ta lashe.

A wannan zabe mai ‘yan takara 17, gwamna mai-ci Rotimi Akeredolu na jam’iyyar APC, na neman wa’adi na biyu yayin da manyan ‘yan adawa EyitayoJegede na Jam’iyyar PDP da kuma Agboola Ajayi na jam’iyyar ZLP ke kalubalantarsa.

Wakilin Muryar Amurka Hassan Umaru Tambuwal da ya yi hira da wasu mazauna birnin Akure da wasu sassan jihar ta wayar tarho, ya ruwaito cewa, an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali.

Ko da yake, wasu kafofin yada labaran kasar sun ce an dan samu ‘yar hatsaniya a karamar hukumar Akure ta Kudu, lamarin da har ya kai ga harba bindiga, amma hukumomin tsaro sun ce babu wanda ya ji rauni.

Sannan akwai rahotanni da ke nuna cewa wasu jam’iyyu na zargin an tafka magudi a zaben.

Hakan na nufin ba kamar yadda aka saba ganin yadda manyan jam’iyyun kasar biyu suke mamaye zabuka ba, a zaben jihar ta Ondo manyan jam’iyyu uku ne suke gwada kaiminsu.

A zaben 2016, gwamna Akeredolu na APC da Mr. Ajayi na jam’iyyar Zenith Labour Party, (ZLP) wanda shi ne mataimakin gwamna Akeredolu, sun ka da Mr Jegede na jam’iyyar PDP.

Amma Ajayi, ya raba gari da gwamna Akeredolu inda ya sauya sheka ya koma ZLP a wannan zabe don kalubalantar tsohon maigidansa.

Rahotanni sun ce tun da misalin karfe 8:30 na safe aka bude rumfunan zabe da dama a sassan jihar ta Ondo mai kananan hukumomi 18.

A kuma lokacin hada wannan rahoto, an rufe da yawa daga cikin rumfunan zaben.

Wannan shi ne karo na biyu da manyan jam’iyyun kasar biyu, wato APC da PDP suke gwada farin jininsu a zaben jihohi wanda wasu masu fashin baki ke cewa zai iya zama manuniya ga abin da zai faru a zaben 2023.

A ranar 19 ga watan Satumba, gwamna mai ci Godwin Obaseki na jam’iyyar PDP ya lashe zaben jihar ta Edo bayan da ya kada abokin karawarsa Osagie Ize-Iyamu na APC.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...