Yadda aka tarwatsa masu zanga-zanga a Kano

BBC

A ranar Asabar ne wasu matasa maza da mata suka shirya wata zanga zanga domin nuna rashin goyon baya kan kirkiro wasu sabbin masarautu a Kano, karkshin kungiyar ”Kano First.”

Masu zanga-zangar sun shirya taruwa ne a harabar Kofar Kwaru da ke gidan sarkin na Kano, daga nan sai su yi tattaki zuwa harabar gidan gwamnatin jihar don nuna rashin goyan bayansu ga yunkurin na gwamnatin.

Toh amma hakan bai yi wu ba sakamakon wasu da ake zargin ‘yan daba ne suka mamaye gurin tun da sanyin safiya dauke da manyan hotunan Sabon Sarkin Bichi Aminu Ado Bayero da na Marigayi Sarki Ado Bayero.

Sakamakon haka ne ya tilasta wa masu zanga-zangar koma wa bakin kotun Kofar Kudu da ke kallon gidan sarkin Kano domin gudanar da taron na su wanda shi ma daga baya aka tarwatsa su.

Nura Ma’aji na daya daga cikin jagororin kungiyar Kano First ya kuma shaida wa BBC cewar:

“Mun fito ne don mu nuna rashin goyon bayanmu kan kirkiro wasu sabbin masarautu a Kano, don ba shi mutanen Kano ke bukata ba, akwai matsalolin da ke damun al’ummar jihar Kano musamman samar da ingantattun kayan more rayuwa, kuma bisa ga fahimtarmu, an tasar wa rusa tarihinmu na masarautun Kano”.

Ya kuma bayyana cewa “ba a nemi ra’ayin mutane ba kawai a ce cikin abin da bai wuce kwana uku ba a ce a gabatar da doka, an yi karatu na biyu, an kuma amince da ita kuma an sa mata hannu, da alama dai akwai lauje cikin nadi wajen gaggawar amincewa da hakan.”

A wani bincike da BBC ta gudanar, ta gano cewa akwai motoci masu dimbin yawa dauke da hotunan gwamnan Kano da kuma mataimakinsa a inda aka ajiye su a wajen Kofar Kwaru ta gidan sarki da tsallaken filin gidan Marigayi Mallam Nasir Kabara, zuwa kofar gidan Kogunan Kano da ke unguwar Jar kasa.

Gwamnatin jihar ta tsayar da ranar Asabar a matsayin ranar da za a mika takardar kama aiki ga sabbin sarakunan da aka kirkiro a jihar ta Kano, duk da cewar wata babbbar kotun jihar a ranar Juma’a ta bayar da umarnin a dakatar da rantsarwar tare kuma da kirkiro wasu masarautu, amma wasu rahotanin sun nuna cewar gwamnatin jihar ta ce bata sami takardar umarnin Kotun ba.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...