Ya kamata a kafa kwamitin da zai binciki ibtila’in bam a kauyen Kaduna, a kuma biya diyya—in ji Sheikh Ɗahiru

Biyo bayan harin bam da aka kai a kauyen Kaduna a wajen bikin Mauludi, malamin addinin Islama, Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya roki gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu da ta kafa kwamitin bincike cikin gaggawa.

A cewarsa, gudanar da cikakken bincike kan tashin bama-bamai na da matukar muhimmanci wajen dakile irin wannan da kan iya faruwa a nan gaba ta hanyar nazarin yanayin da ya haifar da wannan musiba.

Babban malamin addinin Musuluncin kuma jagoran mabiya darikar Tijjaniyya ya yi kira ga gwamnati da ta biya diyya ga iyalan da harin bam ɗin ya rutsa da su a garin Tundun Biri na jihar Kaduna bisa kuskure.

Da yake zantawa da manema labarai a gidansa da ke Bauchi, ya bukaci gwamnatin shugaba Tinubu da ta tabbatar da an yi adalci ga wadanda abin ya shafa tare da hana afkuwar lamarin nan gaba ta hanyar hukunta masu laifi.

More News

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...

Gwamnati za ta fara biyan ma’aikata naira 30,000 mafi ƙarancin albashi a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanar da cewa za su fara aiwatar da tsarin mafi ƙarancin albashi naira 30,000 ga ma'aikatan jihar...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...