Ya kamata ƴan Najeriya su rika addu’a kan kashe-kashen da ake fama da shi—CAN

Kungiyar Kiristocin Najeriya CAN ta bukaci ‘yan Najeriya da su yi addu’a kan kashe-kashen da ake yi a kasar nan tun shekarar 2023.

Shugaban CAN, Archbishop Daniel Okoh, a sakonsa na sabuwar shekara da ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana rashin jin dadinsa kan kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa rayuka sama da 200 a jihar Filato, yana mai cewa ya kamata ‘yan Najeriya su rungumi bambancin al’ummar kasar.

Okoh ya ce ya kamata ‘yan kasar su bar bambance-bambancen kasar su zama ginshikin da za a gina kasa mai karfi da jituwa a tsakanin juna.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]