Kungiyar Kiristocin Najeriya CAN ta bukaci ‘yan Najeriya da su yi addu’a kan kashe-kashen da ake yi a kasar nan tun shekarar 2023.
Shugaban CAN, Archbishop Daniel Okoh, a sakonsa na sabuwar shekara da ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana rashin jin dadinsa kan kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa rayuka sama da 200 a jihar Filato, yana mai cewa ya kamata ‘yan Najeriya su rungumi bambancin al’ummar kasar.
Okoh ya ce ya kamata ‘yan kasar su bar bambance-bambancen kasar su zama ginshikin da za a gina kasa mai karfi da jituwa a tsakanin juna.