An dawo da wutar lantarki a Najeriya, bayan da babban layin wutar lantarkin kasar ya mutu da sanyin safiyar Alhamis.
Lamarin ya janyo katsewar wutar lantarki ga kamfanonin rarraba wutar a fadin Najeriya.
Sai dai kuma an dawo da ita ne bayan an shafe sa’o’i da dama ba tare da ita ba a sassan Najeriyar.
Tun da farko dai kamfanin wutar lantarki (TCN) ya tabbatar da rugujewar babban layin wutar a Najeriya, amma kuma ya tabbatar da cewa ana kokarin shawo kan lamarin.