Wuraren ibada za su cigaba da zama a rufe a jihar Lagos – AREWA News

Gwamnatin jihar Lagos ta ce masallatai da kuma majami’u za su cigaba da zama a rufe duk da umarnin da gwamnatin tarayya ta bayar na sassauta dokar da ta hana bude wuraren ibada.

Da yake magana da yan jaridu a ranar Talata, Kwamishinan harkokin cikin gida, Alofiu Elegushi ya ce bude wuraren ibada a yanzu ba zai yiyu ba saboda jihar ce cibiyar cutar Korona a Najeriya.

Lagos na da mutane 5135 da suka kamu da cutar.

Kwamishinan ya ce gwamnati ta gudanar da tarurruka da dama da shugabannin addini inda suka amince cewa baza a bude wuraren ibada ba har sai komai ya fara dawowa dai-dai.

A taron shugabannin addinan sun tabbatarwa da gwamnati cewa baza su iya tabbatar da kayyade mutanen da za su halarci wuraren ba.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...