Wuraren ibada za su cigaba da zama a rufe a jihar Lagos – AREWA News

Gwamnatin jihar Lagos ta ce masallatai da kuma majami’u za su cigaba da zama a rufe duk da umarnin da gwamnatin tarayya ta bayar na sassauta dokar da ta hana bude wuraren ibada.

Da yake magana da yan jaridu a ranar Talata, Kwamishinan harkokin cikin gida, Alofiu Elegushi ya ce bude wuraren ibada a yanzu ba zai yiyu ba saboda jihar ce cibiyar cutar Korona a Najeriya.

Lagos na da mutane 5135 da suka kamu da cutar.

Kwamishinan ya ce gwamnati ta gudanar da tarurruka da dama da shugabannin addini inda suka amince cewa baza a bude wuraren ibada ba har sai komai ya fara dawowa dai-dai.

A taron shugabannin addinan sun tabbatarwa da gwamnati cewa baza su iya tabbatar da kayyade mutanen da za su halarci wuraren ba.

More News

An ƙona sakatariyar ƙananan hukumomi 2 a jihar Rivers

Wasu da ake kyautata zaton ɓatagari ne sun ƙona wani sashe na sakatariyar ƙananan hukumomin Eleme da Ikwerre dake jihar Rivers. Ƙona ginin na zuwa...

Ƴanbindiga sun hallaka wani shugaban APC a Kebbi

Wasu ‘yan bindiga sun harbe Bako Bala, shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Suru a jihar Kebbi, a yayin wani yunkurin yin garkuwa da...

Kotu ta hana VIO kamawa, tsare motoci ko cin tarar direbobi a kan hanya

Justis Evelyn Maha ta Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta bayar da umarni da ya hana Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa, wanda aka...

Sojojin Najeriya sun hallaka masu haramtacciyar harƙar man fetur

Dakarun runduna ta 6 ta sojojin Najeriya sun kashe wasu mutane biyu da ake zargin barayin man fetur ne, tare da cafke wasu 18...