Wike Ba Ƙaramin Bala’i Ba Ne Ga PDP Kuma Ya Dace a Kore Shi Daga Jam’iyyar—Sule Lamiɗo

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, a matsayin “bala’i” ga jam’iyyar PDP, yana mai kira da a gaggauta a kore shi daga jam’iyyar tare da wasu da ya kira ’yan bogi.

Lamido ya sha alwashin kin halartar kowace ganawar jam’iyyar PDP har sai an cire Wike da sauran wadanda ya ce suna bata jam’iyyar daga ciki. Wannan furuci na Lamido ya zo ne bayan da aka gudanar da taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) na jam’iyyar PDP a Abuja, wanda bai halarta ba.

A wata hira da manema labarai, Lamido ya ce ci gaba da kasancewar Wike a jam’iyyar barazana ce ga zaman lafiya da daidaito a cikin jam’iyyar. “Wike bala’i ne ga jam’iyyar da ta ba shi suna da daraja. Yanzu kuwa yana kokarin ruguzarta,” in ji shi.

Ya bayyana cewa ya ki zuwa taron PDP saboda kasancewar ’yan bogi a ciki, yana mai cewa: “Ni mamba ne na gaskiya a PDP, amma bazan halarci taruka inda ake fakewa da karya ba.”

Lamido ya kuma zargi Ministan na Abuja da hannu wajen rufe hedikwatar PDP da ke Abuja, yana mai cewa hakan cin mutunci ne ga jam’iyyar da ta gina siyasar Wike. “Rufe hedikwatar jam’iyyar da ta baka suna laifi ne, kuma ba al’adarmu ce ba a Najeriya,” in ji Lamido.

Jam’iyyar PDP dai na fama da rikice-rikicen cikin gida tun daga shekarar 2022.

More from this stream

Recomended