Ko a makwannin da suka gabata sai da aka yi wa jami’an lafiya allurar riga-kafin cutar Ebola a kasar
Shugabannin hukumar lafiya ta duniya da hukumar agaji ta MDD sun yi kira a girke sojoji a Jamhuriyar Dimukradiyyar Congo dan bunkasa tsaro ya yin da kasar ke fafutukar yaki da cutar Ebola.
Shugaban hukumar Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce cutar hadari ce ga rayuwar jama’a.
Shi ma babban mai kula da ayyukan jin kai da tabbatar da zaman lafiya na MDD Jean-Pierre Lacroix, ya na fatan za a shawo matsalar tsaro a kasar dan maida hankali kan birnin Beni wadda ita ce cibiyar cutar Ebola.
Sama da mutane 300 ne suka kamu da cutar, wasu 190 suka mutu, an kuma killace sama da 5000, a gabashin Jamhuriyar Dimkradiyyar Congo a barkewar cutar Ebola ta baya-bayan.