Watakila Juanma Lillo ya zama mataimakin Guardiola

Juanma Lillo

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Watakila Juanma Lillo ya kama aikin mataimakin Guardiola a Manchester United, bayan da ya bar aikin horar da Qingdao Huanghai ta China.

Dan kasar Spaniya ya yi nasarar kai Qindao babbar gasar China a kakar bara, amma yanzu wasu rahotanni na cewar zai yi aikin mataimakin koci a gasar Premier League.

Kamar yadda Daily Mail da Daily Mirror suka wallafa kocin yana da kwarewar da zai daga martabar Manchester City a wasannin kwallon kafa.

Guardiola bai da mataimaki tun bayan da Mikel Arteta ya karbi aikin jan ragamar Arsenal a cikin watan Disamba.

Wasu da aka sa ran za su maye gurbin Arteta a Etihad sun hada da Xabi Alonso da Vincent Kompany da sauran fitattun masu horar da tamaula.

Lillo ya tabbatar da barin kungiyar ta China wadda ya bai wa dalilin cewar zai je ya kula da mahaifiyarsa wadda ke fama da jinya.

Guardiola ya taka kwallo a karkashin Lillo a kungiyar Dorados ta Mexico daga nan ya yi ritaya daga taka-leda.

Lillo ya horar da Tolosa CF da Mirandes da Cultural Leonesa da UD Salamanca da Real Oviedo da Tenerife da Real Zaragoza da Ciudad Murcia.

Sauran kungiyoyin da ya ja ragama sun hada da Terrassa da Dorados da Real Sociedad da Almeria da Millonarios da Atletico Nacional da kuma Vissel Kobe.

Ya kuma yi aikin mataimaki a tawagar kwallon kafar Chile da kuma Sevilla mai buga gasar La Liga ta Spaniya.

Ranar 17 ga watan Juni za a ci gaba da gasar Premier, inda Manchester City za ta buga kwanatan wasa da Arsenal.

A kuma ranar za a kece raini tsakanin Aston Villa da Sheffield United.

Manchester City tana mataki na biyu a teburin Premier da tazarar maki 25 tsakaninta da Liverpool ta daya tun bayan da aka dakatar da wasanni a cikin watan Maruis saboda bullar cutar korona.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...