Wata tifar yashi ta kashe mutum guda tare da jikkata wasu da dama  Jalingo

Akalla mutum guda ya rasa ransa wasu da dama kuma sun jikkata bayan da wata motar tifa dake dauke da yashi ta kwace daga kan titi tayi cikin kasuwar Mile 6 dake Jalingo babban birnin jihar Taraba.

Wani shedar gani da ido ya fadi cewa motar ta kwace daga hannun direban ta ne bayan da tayarta ta fashe lokacin da take tsaka da falfala gudu.

“Ya faru cikin sauri motar tana tsaka da falfala gudu sai taya ta fashe direban ya kasa sarrafa ta kawai sai tayi cikin mutane,” a cewar wani mai sayar da kaya a wurin da lamarin ya faru.

Jami’an bada agajin gaggawa da suka hada da yan sanda da jami’an kiwon lafiya sun yi gaggawar isa wurin inda suka garzaya da wadanda suka jikkata ya zuwa asibiti.

More from this stream

Recomended