Wata Mata Ta Watsa wa Mijinta Ruwan Zafi Saboda Yaƙi Zuwa Da Ita Bikin Abokinsa

Rundunar yan sandan jihar Lagos ta ce wata mata mai suna, Dorcas Oluwabukola ta shiga hannun yan sanda bayan da aka zargeta da watsawa mijinta ruwan zafi biyo bayan sabani da suka samu.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Lagos, Benjamin Hundeyin shi ne ya bayyana haka ranar Litinin a cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN.

Hundeyin ya ce lamarin ya faru ne ranar 18 ga watan Disamba.

Ya ce wacce ake zargin ta tafasa ruwan zafi ta watsawa mijin nata kan zargin cewa yaki zuwa da ita wurin bikin abokinsa.

Ya kara da cewa a ranar ne aka kama matar bayan sa ofishin yan sanda na Meiran ya samu labarin faruwar lamarin.

More News

An kama mutane biyu  masu garkuwa da mutane a jihar Kogi

Wasu ɓatagari biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne jami'an ƴan sanda da haɗin gwiwar ƴan bijilante suka kama a garin Ibobo-Abocho...

Jirgi mai saukar ungulu ya yi hatsari a Akwa Ibom

Wasu ma'aikatan kamfanin haƙar man fetur su 6 da kuma matuƙan jirgi su biyu su mutu a wani hatsarin jirgi mai saukar ungulu a...

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naɗa

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...