Wataƙila a buɗe iyakar Najeriya da Kotono

Masu jigilar kaya da ke aiki a iyakar Seme sun rubutawa gwamnatin tarayya wasika suna bukatar a bude kan iyakoki domin shigo da motoci.

Daraktan Sufuri na Ma’aikatar Sufuri ta Tarayya, Ibrahim Musa ne ya bayyana haka a Seme yayin wani taro tsakanin jami’an Najeriya da Benin da kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ta shirya.

Ya bayyana cewa masu jigilar kayayyaki sun yi kira ga tsohon karamin ministan sufurin jiragen sama a ziyararsa ta karshe da ya kai kan iyakar, inda ya nemi a sake farfado da iyakar.

Ya ce takardar da aka shirya aka aika zuwa ga gwamnatin tarayya bisa wannan bukata majalisar zartarwa ta tarayya ta amince da ita.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]