Wani jami’in kwastam ya harbe kansa har lahira a Kano

Wani jami’in hukumar kwastam ya harbe kansa har lahira a gidansa dake unguwar Farm Centre a cikin birnin Kano.

Mai magana da yawun rundunar Æ´an sandan jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

Kiyawa ya ce jami’in mai suna Abdullahi Magaji na aiki ne a hedkwatar hukumar ta kwastam dake Abuja ana zargin cewa ya kashe kansa ne a ranar 06 ga watan Mayu.

Babban baturen Æ´an sanda na Farm Centre shi ne ya jagoranci jami’an Æ´an sanda ya zuwa gidan da abun ya faru.

Tuni dai kwamishinan Æ´an sandan jihar, Mohammed Usaini Gumel ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautun jihar

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautun jihar ya kuma sanar da sake naÉ—a, Muhammad Sanusi a matsayin...

Sanusi ya sake zama Sarkin Kano

Shekaru hudu bayan sauke Muhammadu Sanusi II daga matsayin Sarkin Kano, Gwamna Abba Yusuf, na jihar Kano ya mayar da shi kan karagar mulki.Gwamnan...

Kotu ta ba da belin Abba Kyari

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da belin tsohon kwamandan rundunar ‘yan sandan farin kaya DCP Abba Kyari na tsawon makonni...

Tinubu zai halarci bikin rantsar da shugaban ƙasar Chadi

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu zai halarci bikin rantsar da shugaban ƙasar Chad, Mahamat Deby. A wata sanarwa da Ajuri Ngelale mai magana da yawun...