Wasu Mazauna Birnin Kebbi Sun Wawushe Kayan Abinci A Rumbun Ajiyar Gwamnati

Wasu mazauna jihar Kebbi sun kai farmaki rumbun ajiye kayan abinci na gwamnati dake yankin Bayan Ƙara a Birnin Kebbi  a daren ranar Asabar inda suka sace kayan abinci.

Ɓatagarin wanda suka fi ƙarfin jami’an tsaro da aka a jiye a wurin ajiye kayayyakin sun kuma farfasa wasu wuraren ajiyar kayayyaki da kuma shaguna na mutane inda suka yi musu satar kayan abinci.

Sun kuma sace kayan abinci dake cikin wata mota da ta lalace wanda za a rabawa mutane a birnin Kebbi.

Hare-hare kan ɗakunan ajiye kayan abinci ya faru a garin Suleja dake jihar Niger da kuma babban birnin tarayya Abuja..

Da yake magana da wakilin jaridar Daily Trust shugaban kungiyar masu sayar da kayan abinci a kasuwar ta Bayan Kara dake birnin Kebbi ya ce matasan sun ƙone shaguna da kuma wuraren ajiye kayan abinci.

“Su jami’an tsaro sun yi harbin iska da kuma na barkonon tsohuwa amma su matasan ba su tsorata ba sai da suka kutsa kai suka kwashe kayan abincin dake rumbun  a jiyar gwamnati da kuma wasu daga cikin shagunan mu.”

More News

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...