Wasu matasa uku da ake zargi da garkuwa da mutum sun gurfana a gaban kotu a Kano

Wasu matasa guda uku sun bayyana a gaban wata kotun majistire dake zamanta a unguwar Gyadi-Gyadi dake Kano inda ake tuhumarsu da zargin  yin garkuwa da mutane.

Ana zarginsu ne da yin garkuwa da Muhammad Nasir wani yaro mai shekaru 4 kuma suka buƙaci a biya su dala $180 a matsayin kuɗin fansa..

Amma kuma jami’an tsaro suka bi diddiginsu suka kama su.

Waɗanda ake zargin Hizbullah Salisu, Aliyu Abubakar da kuma  Hassan Aliyu an tuhume su da laifin haɗabaki, aikata laifi da kuma yin garkuwa da mutum.

Alƙaliyar kotun Rakiya Lami Sani ta bada umarnin a tura su gidan gyaran hali bayan da suka ƙi amsa laifin da ake tuhumarsu.

More News

EFCC ta kama tsohon gwamnan Taraba Darius Ishaku

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta kama Darius Ishaku tsohon gwamnan jihar Taraba kan zargin al-mundahanar kuɗaɗen...

Kotu ta tsare matashi kan zargin lalata da yarinya Æ´ar shekara 13

Kotun majistare ta Badagry da ke Legas a ranar Alhamis, ta bayar da umarnin tsare wani matashi dan shekara 28, Stanley Amos, da ake...

Kotu ta É—aure waÉ—anda suka yi fashi a bankin Offa da ke jihar Kwara a 2018

Mai shari’a Haleemah Salman ta babbar kotun jihar Kwara da ke zamanta a Ilorin a jiya ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga...

Gwamnatin Najeriya ta kara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC ‘alawee’ zuwa N77,000

Gwamnatin tarayya ta kara yawan alawus din masu yi wa kasa hidima (NYSC) zuwa N77,000 duk wata, daga Yuli 2024.  Wannan ci gaban ya...