Wasu gwamnonin PDP sun kauracewa yakin neman zaben gwamnan Osun

Jam’iyar PDP a ranar Alhamis ta gudanar da taron gangamin yakin neman zabe a jihar Osun gabanin zaɓen gwamnan jihar gwamnan jihar da za ayi.

Za a gudanar da zaɓen gwamnan jihar ranar Asabar 16 ga watan Afrilu.

An gudanar da taron yakin neman zaben ne a Osogbo babban birnin jihar inda jam’iyar ta bukaci a zabi dan takarar ta Ademola Adeleke.

Taron gangamin ya samu jagoranci ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Atiku Abubakar da kuma shugaban jam’iyyar Iyorchia Ayu.

Sauran waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Abubakar Bukola Saraki da gwamnan jihar Sokoto,Aminu Waziri Tambuwal, na Bayelsa,Douye Diri, Godwin Obaseki na Edo, da kuma Ifeanyi Okowa na jihar Delta.

Sai dai wasu daga cikin gwamnonin jam’iyar sun kauracewa taron kamar na jihar Rivers,Nyesom Wike, Samuel Ortom na jihar Benue, Seyi Makinde na jihar Oyo, Ikpeazu Okezie na jihar Abia da kuma Ifeanyi Ugwuanyi na jihar Enugu.

Ana ganin dai kauracewar ta su nada nasaba da rikicin da ya biyo bayan zaɓen mataimakin shugaban kasa da Atiku Abubakar yayi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]