Wasu gwamnonin PDP sun kauracewa yakin neman zaben gwamnan Osun

Jam’iyar PDP a ranar Alhamis ta gudanar da taron gangamin yakin neman zabe a jihar Osun gabanin zaÉ“en gwamnan jihar gwamnan jihar da za ayi.

Za a gudanar da zaɓen gwamnan jihar ranar Asabar 16 ga watan Afrilu.

An gudanar da taron yakin neman zaben ne a Osogbo babban birnin jihar inda jam’iyar ta bukaci a zabi dan takarar ta Ademola Adeleke.

Taron gangamin ya samu jagoranci É—an takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Atiku Abubakar da kuma shugaban jam’iyyar Iyorchia Ayu.

Sauran waÉ—anda suka halarci taron sun haÉ—a da Abubakar Bukola Saraki da gwamnan jihar Sokoto,Aminu Waziri Tambuwal, na Bayelsa,Douye Diri, Godwin Obaseki na Edo, da kuma Ifeanyi Okowa na jihar Delta.

Sai dai wasu daga cikin gwamnonin jam’iyar sun kauracewa taron kamar na jihar Rivers,Nyesom Wike, Samuel Ortom na jihar Benue, Seyi Makinde na jihar Oyo, Ikpeazu Okezie na jihar Abia da kuma Ifeanyi Ugwuanyi na jihar Enugu.

Ana ganin dai kauracewar ta su nada nasaba da rikicin da ya biyo bayan zaɓen mataimakin shugaban kasa da Atiku Abubakar yayi.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...