Wani sojan ruwan Najeriya ya hallaka abokin aikinsa a Zamfara

Hedikwatar Tsaron Najeriya ta kama wani sojan ruwa mai suna A. Akila bisa zarginsa da kashe abokin aikinsa.

An tura Akila zuwa sansanin Forward Operating Base Dansadua domin aikin Operation Fansan Yamma, inda ake zargin ya kashe abokin aikinsa a wani yanayi mai cike da tambayoyi.

Lamarin ya faru da sanyin safiyar Juma’a a jihar Zamfara.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, Daraktan Ayyukan Watsa Labaran Tsaro, Manjo Janar Buba Edward, ya ce sojan ruwan ya harbi abokin aikinsa sau da dama.

Buba ya ce, “A ranar 25 ga Oktoba, 2024, da misalin karfe 3:12 na safe, wani jami’in sojan ruwa, LS Akila A., wanda aka tura zuwa FOB Dansadua domin Operation FANSAN YAMMA, a wani yanayi mai cike da tambayoyi, ya bude wuta ba kakkautawa ya kashe abokin aikinsa.

“Daga nan aka kama shi, aka kwace masa makami, aka kuma tsare shi, kuma bincike ya fara kan lamarin. Bayan kammala bincike, za a mika shari’ar a gaban kotun soji da aka tanada domin magance irin wadannan laifuka a tsakanin dakarun tsaro.”

More News

Kotu ta bada umarnin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Kano

Wata babbar kotu a jihar Kano ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar wato KANSIEC da ta cigaba da shirye-shiryen gudanar da...

Kotu ta bada umarnin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Kano

Wata babbar kotu a jihar Kano ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar wato KANSIEC da ta cigaba da shirye-shiryen gudanar da...

Ministan tsaro Badaru ya yaba wa gwamnan Zamfara saboda tallafa wa aikin soji a jihar

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya jinjina wa Gwamna Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da tallafa wa ayyukan soji a Jihar Zamfara.Ministan...

An kama mutane biyu  masu garkuwa da mutane a jihar Kogi

Wasu ɓatagari biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne jami'an ƴan sanda da haɗin gwiwar ƴan bijilante suka kama a garin Ibobo-Abocho...