Wani soja ya harbe kansa har lahira a jihar Ogun

Wani sojan rundunar sojan Najeriya, ya kashe kansa a Abeokuta babban birnin jihar Ogun.

Sojan mai suna, Boyi Thankgod yana aiki ne da Atileri birget ta 35 dake Alamala a Abeokuta babban birnin jihar ta Ogun.

Jaridar Daily Trust ta gano cewa sojan ya harbe kansa ne a wurin bikin tunawa da yan mazan jiya da aka gudanar.

Wani hoto marar dadin kalla ya nuna gawar marigayin kwance cikin jini yayin da kansa ya fita daga gangar jikinsa saboda karfin harbin bindigar.

“Kwarai gaskiya ne lamarin ya faru jiya ranar ( Litinin) ” kamar yadda wata majiya dake barikin ta fadawa jaridar Daily Trust.

Majiyar ta ƙara da cewa ana cigaba da bincike domin gano dalilin da yasa sojan ya kashe kansa.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...