Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa zargin kashe mahaifiyarsa mai suna Aminat, wadda aka ce tana da shekaru kusan 100 a duniya, biyo bayan wata takaddama kan kudin da aka sayar da kwakwar manja.

Wani ganau mai suna Rasaki ya shaida a ranar Lahadi cewa Lukman da mamaciyar sun dauki wani lebura ne wanda ya taimaka musu wajen sayar da wasu ƴaƴan kwakwar.

Yayin da ma’aikaciyar ke son mika kudin, an ruwaito marigayiya Aminat ta dage cewa sai an ba da kudin ta hannunta, lamarin da ya harzuka ɗan nata.

Ya ci gaba da cewa, “Mutanen kauyen duk sun ji takaici da muka samu labarin faruwar lamarin.  Lamarin ya faru ne a kauyen Kajola da ke kusa da Apomu ranar Asabar da misalin karfe hudu na yamma.”

More News

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naɗa Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...