Wani Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Bayan Da Taki Bashi ₦10,000

Rundunar yan sandan jihar Rivers, ta kama wani matashi mai suna Osaro Owate kan zargin kisan mahaifiyarsa a unguwar Elesa dake karamar hukumar Eleme ta jihar.

Matashin ya aikata kisan kan ne bayan da sabani ya shiga tsakaninsu kan naira 10,000

Wanda ake zargin dai yayi ikirarin cewa yana fama da cutar aljanu sama da shekaru 30 ya amince da yin amfani da fatanya wajen kisan mahaifiyar.

Da yake magana cikin wani fefen bidiyo da aka naɗa Owate ya ce ya faɗa mahaifiyarsa taje banki ta ciro kuɗi domin ta bashi ₦20,000 ya sayi kayan da zai saka a wajen wani bikin mutuwa amma a maimakon haka sai kawai ta bashi 10,000 abin da ya jawo cacar baki har ta kai ga ya kashe ta.

More News

Wani sojan ruwan Najeriya ya hallaka abokin aikinsa a Zamfara

Hedikwatar Tsaron Najeriya ta kama wani sojan ruwa mai suna A. Akila bisa zarginsa da kashe abokin aikinsa.An tura Akila zuwa sansanin Forward Operating...

Kotu ta bada umarnin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Kano

Wata babbar kotu a jihar Kano ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar wato KANSIEC da ta cigaba da shirye-shiryen gudanar da...

Kotu ta bada umarnin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Kano

Wata babbar kotu a jihar Kano ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar wato KANSIEC da ta cigaba da shirye-shiryen gudanar da...

Ministan tsaro Badaru ya yaba wa gwamnan Zamfara saboda tallafa wa aikin soji a jihar

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya jinjina wa Gwamna Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da tallafa wa ayyukan soji a Jihar Zamfara.Ministan...