Wani kason na yan majalisar wakilai za su fice daga jam’iyar APC

[ad_1]








Abdulrazak Atunwa, guda cikin yan majalisar wakilai 37 da suka sauya sheka daga jam’iyar APC ya ce akwai karin wasu yan majalisar da za su fice daga jam’iyar.

Atunwa wanda ya koma jam’iyar PDP ya ce sauya shekar tasu kason farko ne cikin jerin mambobin majalisar da za su fice daga jam’iyar.

Ya ce jama’a su sa ran cewa mambobi da dama sun nuna sha’awarsu ta fita daga jam’iyyar.

Atunwa ya ce APC jam’iya ce da dukkaninsu sukai aikin ginata lokacin da mutane suka fito daga sauran jam’iyu daban-daban su kai yakin neman zabe suka kuma kafa gwamnati.

Dan majalisar ya ce abin takaici bayan da aka rantsar da gwamnati a watan Mayun shekarar 2015 jam’iyar ta kauce daga kan turbar da aka kafata.

Atunwa ya kara da cewa masu sauya shekar suna son cigaba tattalin arzikin kasa da kuma girmama doka da oda.




[ad_2]

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...