Uwargidan Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu, Ta Samu Sarautar Gargajiya a Jihar Enugu

Uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta samu karramawar sarautar gargajiya daga Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Enugu, inda aka ba ta sarautar ‘Ugosimba 1 of Enugu’, wato “Lu’ulu’u ko Shaƙin Dawisu daga wata masarauta.”

An ba ta wannan sarauta ne a ranar Talata yayin wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu da ta kai jihar. Shugaban majalisar sarakunan, Igwe Ikechukwu Asadu, ya bayyana cewa sarautar wata hanya ce ta nuna godiya ga irin gudummawar da Sanata Remi Tinubu ke bayarwa a fannin jin ƙai, kiwon lafiya da kuma ci gaban ƙasa gaba ɗaya.

“Kin yi wa majalisar dattawa hidima na tsawon wa’adin shekaru goma sha biyu (12), kuma an ba ki lambar yabo ta Commander of the Order of Niger (CON). Amma bayan siyasa ma, muna jin daɗin ganin yadda kike taimaka wa marasa galihu, da ƙarfafa masu jinya da ma’aikatan asibitoci kamar nas da ungozoma,” in ji Igwe Asadu.


A jawabinta na karɓar wannan gagarumar sarauta, Oluremi Tinubu ta bayyana godiya ƙwarai, tana mai cewa ta ji nutsuwa da salama tun lokacin da ta sauka a jihar Enugu.

“Wannan karramawa ba ta tsaya kaina kadai ba, har da maigida na, shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma danginmu gaba ɗaya,” in ji ta.

“Zan riƙe wannan sarauta tamkar zinariya, kuma zan ci gaba da tuna Jihar Enugu da alheri. Lallai jihar nan na da kwanciyar hankali kuma mutane masu ƙauna da mutunci.”

More from this stream

Recomended