UAE ta kawo ƙarshen dokar hana ƴan Najeriya biza bayan Tinubu ya kai ziyara Abu Dhabi

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi nasarar kulla wata yarjejeniya mai cike da tarihi tsakanin Najeriya da Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), wanda ya kawo karshen dokar hana bizar da ta yi wa ƴan Najeriya.

An samu nasarar ne a ziyarar da shugaba Tinubu ya kai Abu Dhabi, bayan halartar taron kasashen G-20 da ya gudana a kasar Indiya.

Muhimmin abin ya faru ne lokacin da Ambasada Designate, Amb Salem Saeed Al-Shamsi, ya gabatar da wasiƙarsa ga shugaba Tinubu a Aso Rock, Nijeriya.

Shugaban kasar bai bata lokaci ba wajen jagorantar warware takaddamar diflomasiyya da ta dade tana wanzuwa.

Mai magana da yawun shugaban kasar, Cif Ajuri Ngelale, ya bayyana cikakken bayanin yarjejeniyar a cikin wata sanarwa a ranar Litinin, yana mai bayyana ganawar da mahukuntan UAE a matsayin mai matukar fa’ida.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...