Tinubu zai halarci taron tattalin arziki a kasar Saudiya

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu zai halarci taron ƙasar Saudiya da kasashen Afrika da kuma taron kasashen Larabawa da na Afrika da za ayi a birnin Riyadh na kasar Saudiya.

Tarukan biyu za a gudanar da su ranar 10 da 11 ga watan Nuwamba.

A wata sanarwa ranar Lahadi, Ajuri Ngelale mai magana da yawun shugaban ƙasa ya ce Tinubu zai halarci taron a wani bangare na ƙoƙarin da yake na samun karin kwararowar kuɗade wajen cikin tattalin arzikin Najeriya.

Ya ce Tinubu zai jagoranci ƙoƙarin da Afrika take na amfana daga yarjejeniyar AFCTA ta kasuwancin bai ɗaya a nahiyar.

A taron za a tattauna batutuwa da dama kan tattalin arziki da suka shafi nahiyoyin biyu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...