Tinubu zai halarci bikin rantsar da shugaban ƙasar Chadi

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu zai halarci bikin rantsar da shugaban ƙasar Chad, Mahamat Deby.

A wata sanarwa da Ajuri Ngelale mai magana da yawun shugaban ƙasar ya fitar ranar Laraba ya ce Tinubu zai ta shi daga Abuja ya zuwa N’Djamena babban birnin ƙasar Chad a ranar Alhamis kuma zai dawo bayan kammala bikin.

Deby wanda ya kasance shugaban riƙo na kasar an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na ranar 6 ga watan Mayu bayan da majalisar tsarin mulki ƙasar ta tabbatar da shi.

Majalisar ta ayyana Deby a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan da tayi watsi da ƙorafin ƴan takarar shugaban ƙasa biyu Success Masara da kuma Albert Padacke.

Ngelale ya ce Tinubu zai samu rakiyar manyan jami’an gwamnati.

More News

Shan giya na halaka sama da mutum miliyan 2.6 duk shekara—WHO

Wani rahoton Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), ya nuna cewar shan giya na kashe mutum miliyan 2.6 a duk shekara. Rahoton ya ƙara da cewa...

Ƴan fashin daji sun kashe ƴan bijilante 4 da ɗan sanda ɗaya a Kaduna

Wasu da ake zargin ƴan fashin daji ne sun kai farmaki mazaɓar Kakangi dake ƙaramar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna inda suka kashe...

Ƴan Boko Haram sun yi garkuwa da wani alƙali da matarsa a jihar Borno

Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun yi garkuwa da alƙalin babbar kotu mai Shari'a, Haruna Mshelia tare da matarsa da kuma dogarinsa. Rahotanni sun bayyana cewa...

Abdul Aziz Yari ya dauki nauyin karatun dalibai 1,700 a Jihar Zamfara

Tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma sanata mai wakiltar mazabar Zamfara ta yamma, Abdulaziz Yari Abubakar, ya baiwa 'yan asalin jihar 1,700 tallafin karatu a...