Tinubu Zai Gana Da Shugabannin Kasashen ECOWAS Akan Juyin Mulkin Niger

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Bola Ahmad Tinubu zai jagoranci taron shugabannin kungiyar ECOWAS a Abuja kan juyin mulkin kwanannan da aka yi a Jamhuriyar Nijar.

Mai bawa shugaban kasa shawara kan sadarwa, Dele Alake shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

A daren ranar Laraba ne, Kanal Amadou Abdramane ya sanar da sauke shugaban kasa, Mohamed Bazoum daga kan kujerarsa.

Taron na ranar Lahad 30 ga watan Yuli zai gudana ne a Abuja.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]