Tinubu ya ziyarci wadanda suka jikkata a harin Benue

A ranar Laraba ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ziyarci mutanen da su ka jikkata a mummunan harin da wasu mutane su ka kai garin Yelewata dake karamar hukumar Guma ta jihar Benue.

Harin wanda aka kai ranar Asabar ya halaka akalla mutane sama da 100 a yayin da wasu da dama suka jikkata.

Tinubu ya sauka filin jirgin saman sansanin sojan Najeriya dake Benue da misalin karfe 12:48 na rana.

Da ga nan shugaban ya wuce asibitin koyarwa na jihar Benue inda wasu daga cikin wadanda suka jikkata ke jinya.

A yayin ziyarar Tinubu ya samu rakiyar gwamnan jihar Hyacinth Alia da wasu manyan jami’an gwamnati.

Bayan duba marasa lafiyar shugaban ya halarci wani taron masu ruwa da tsaki a jihar.

More from this stream

Recomended