Tinubu Ya Sasanta Gwamna Fubara Da Minista Wike

Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sasanta rikicin siyasa da ya dabaibaye Gwamnan Jihar Ribas, Siminilayi Fubara, da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike.

Fadar shugaban ƙasa ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da aka fitar, tana mai cewa sulhun ya biyo bayan zaman sasanci da shugaban ƙasar ya jagoranta domin kawo ƙarshen rikicin da ya dade yana tayar da kura a jihar.

Tsohon gwamnan jihar Ribas kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce an cimma matsaya, inda ya bayyana cewa: “Komai ya wuce, mun amince mu yi aiki tare saboda mu ‘yan uwan juna ne.”

Gwamna Siminilayi Fubara ma ya bayyana ra’ayinsa na goyon bayan zaman lafiya, inda ya ce: “Abin da Jihar Ribas take buƙata shi ne zaman lafiya kuma za mu yi komai don tabbatar da hakan.”

Tun a baya, rikicin siyasar ya kai ga wasu matakai na doka, ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci da dakatar da gwamnan daga wasu muhimman ayyuka na tsawon wata shida.

Shugaba Tinubu ya bukaci dukkan ɓangarorin da su rungumi zaman lafiya da haɗin kai domin ci gaban jihar da ƙasar gaba ɗaya.

More from this stream

Recomended