Shugaba Bola Tinubu ya sanar da karin albashi na wucin gadi na watanni shida ga wasu ma’aikata a kasar.
Shugaban kasar ya sanar da karin ne a jawabinsa na bikin cikar ‘yancin kai na farko a ranar Lahadi.
Karin albashin dai shi ne zai taimaka wajen dakile radadin cire tallafin man fetur, wanda ya haifar da tsadar rayuwa a kasar.
“Bisa tattaunawar da muka yi da ma’aikata, ‘yan kasuwa da sauran masu ruwa da tsaki, muna bullo da karin albashin na wucin gadi domin inganta mafi karancin albashi na tarayya ba tare da haifar da hauhawar farashin kayayyaki ba,” in ji Tinubu.
“Na tsawon watanni shida masu zuwa, matsakaitan ma’aikata za su rika samun karin Naira Dubu Ashirin da Biyar a kowane wata.”