Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya naÉ—a Dr. Olayemi Michael Cardoso a matsayin sabon gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) na tsawon shekara biyar.
Naɗin nasa zai fara aiki ne da zarar Majalisar Dattijan ƙasar ta amince da shi.
Wannan bayani na Æ™unshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Æ™asar, Ajuri Ngelale ya fitar, yau Juma’a.
Bayanin ya ce shugaban ƙasar ya ɗauki matakin ne bisa dogaro da sashe na 8 (1) na dokar Babban Bankin Najeriya ta 2007, wadda ta bai wa shugaban ƙasar karfin ikon naɗa shugaba da mataimaka huɗu na Babban Bankin.
Sanarwar ta kuma bayyana sunayen wasu mutane huÉ—u da shugaban ya amince da su domin naÉ—awa a matsayin mataimakan gwamnan babban bankin na Najeriya.