Tinubu ya naɗa shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa da sakataren gwamnatin tarayya

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya naɗa kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila a matsayin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa.

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa, Ibrahim Hassan Hadejia shi ne zai kasance mataimakin shugaban ma’aikatan fadar ta shugaban kasa.

Har ila yau Tinubu ya naɗa tsohon gwamnan jihar Benue, George Akume a matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya.

Wannan ne naɗe-naɗe na farko da shugaban kasar ya fara yi tun bayan da aka rantsar da shi a ranar Litinin 29 ga watan Mayu.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Yan sanda sun gano haramtacciyar masana’antar ƙera makamai Cross River

Rundunar yan sandan jihar Rivers ta ce ta bankaɗo wata haramtacciyar masana'antar ƙera bindigogi da nakiyoyi dake garin Osomba a karamar hukumar Akamkpa ta...