Tinubu ya haɗu da Okonjo-Iweala, Shugabar WTO

Shugaba Bola Tinubu yana ganawa da Ngozi Okonjo-Iweala, Darakta Janar ta kungiyar kasuwanci ta duniya WTO a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Okonjo-Iweala ta isa fadar shugaban kasa ta Villa tare da tsohon karamin ministan lafiya, Dr. Ali Pate da misalin karfe 2:50 na yammacin ranar Talata.

Kawo yanzu dai ba a san makasudin taron ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Ku tuna cewa Okonjo-Iweala a farkon watan Yuni ta gana da Tinubu a lokacin da dukkansu suka halarci taron shugabannin da aka gudanar a birnin Paris na kasar Faransa.

Okonjo-Iweala ita ce ministar kudi a zamanin gwamnatin tsohon shugaban kasa Good luck Jonathan.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...