Tinubu ya gana da tsohon sarkin Kano Sanusi

Shugaban kasa Bola Tinubu ya gana da tsohon Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi a ranar Alhamis.

Tinubu ya gana da Sanusin ne a fadar shugaban kasa a ranar Alhamis.

Da misalin karfe 5 na yamma ne tsohon gwamnan babban bankin Najeriya CBN ya isa fadar shugaban kasar domin ganawa da Tinubu, har yanzu ba a bayyana ajanda a taron ba.

Ziyarar ta Sanusi ta zo ne bayan da Tinubu ya dakatar da tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya Godwin Emefiele.

Tinubu da Sanusi suna ganawa a karon farko tun bayan da ya dare kujerar shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu.

More from this stream

Recomended