Tinubu ya gana da Abdullahi Adamu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da tsohon shugaban shugaban jam’iyar APC, Abdullahi Adamu da kuma tsohon sakataren jam’iyar, Iyiola Omisore a fadar Aso Rock dake Abuja.

Mutanen biyu sun sauka daga kan mukamansu gabanin taron kwamitin zartarwar jam’iyar APC da aka shirya gudanarwa a baya kuma aka dage taron.

Shugaba Tinubu wanda shi ne jagoran jam’iyar baki daya yana da fada aji a cikin jam’iyar APC kuma ana sa ran zai taka muhimmiyar rawa wajen zaÉ“en sabbin shugabannin jam’iyar.

Babu wata sanarwa kan dalilin ziyarar da suka kai amma ana ganin baya rasa na saba da warware rikicin da ya dabaibaye jam’iyar.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...