Tinubu ya dawo daga Saudiya

Bola Ahmad Tinubu, dan takarar shugaban kasa a jam’iyar APC ya dawo gida Najeriya a jiya Lahadi daga kasar Saudiya inda yayi aikin Umrah.

Tinubu ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja.

Gwamnan jihar Jigawa, Muhammad Badaru Abubarkar na daga cikin mutanen da suka tarbe shi a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja.

More from this stream

Recomended