Tinubu Ya Ce Zai Ziyarci Jihar Benue Ranar Laraba

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa zai soke duk wasu ayyuka da ke cikin jadawalin aikinsa domin kai wa al’ummar Jihar Benue ziyarar jaje a ranar Laraba mai zuwa.

Wannan sanarwar ta fito ne a ranar Litinin, 16 ga Yuni, 2025, jim kaɗan bayan kisan da aka yi wa fiye da mutane 250 a Yelewata, ƙaramar hukumar Guma ta jihar.

Rahotanni sun bayyana cewa shugaban ya fuskanci suka daga al’umma bisa abin da da dama suka kira da jinkiri da sakaci wajen nuna damuwa da halin da mutanen Benue ke ciki. A cewar wasu daga cikin ‘yan Najeriya, shugaban bai kai ziyarar gani da ido ga yankin ba duk da munin lamarin.

A cewar Tinubu: “Zan soke duk wani abu da ke cikin jadawalin aikina domin kai ziyarar jaje ga mutanen Benue a ranar Laraba.”

Zuwa yanzu, gwamnan Jihar Benue, Reverend Father Hyacinth Alia, ya bayyana cewa wasu ‘yan siyasa da ke cikin majalisar tarayya na da hannu a kai hare-haren da ake wa al’ummar jihar. Haka kuma, wasu rahotanni sun nuna cewa an kama mutum 33 a Makurdi dangane da wannan al’amari.

A halin da ake ciki, akwai ƙara yawaitar kira daga sassa daban-daban na ƙasa, da ke neman gwamnatin tarayya ta ɗauki matakin gaggawa domin magance tashe-tashen hankulan da ke kara jefa al’ummar Benue cikin fargaba da tashin hankali.

Karin bayani zai biyo baya…

More from this stream

Recomended