Tinubu: Ba Za Mu Bari Rashin Tsaro Ya Durƙusar Da Ƙoƙarin Gwamnati Ba

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta bari matsalar tsaro ta hana ƙoƙarin da take yi na magance rashin tsaro a sassan ƙasar ba, tare da tabbatar da inganta tsaro da walwalar al’umma.

Ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi lokacin da mataimakinsa da ƙungiyar gwamnonin Najeriya suka kai masa ziyarar gaisuwar Sallah a gidansa da ke Legas.

Tinubu ya ce, “tattaunawar da na yi a lokacin ziyarar aiki da na kai Birtaniya ta mayar da hankali ne kan tsaro da jin daɗin al’umma, tare da nemo hanyoyin samun kayan aiki da tallafi daga ƙasashen waje.”

Ya kuma ƙara da cewa ya tattauna da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, kan yiwuwar haɗin gwiwa wajen samar da kayan tsaro da tallafi.

Shugaban ya ce, “gwamnati na ƙoƙarin ƙarfafa alaƙa da sauran ƙasashe domin inganta tsaro,” yana mai jaddada cewa rashin tsaro babbar barazana ce ga ci gaba da walwalar ƙasa.

Haka kuma, ya yi gargaɗi kan tasirin rikicin Gabas ta Tsakiya ga tattalin arziƙin ƙasa, musamman yadda yake haifar da hauhawar farashin man fetur da kuma rage ƙarfin saye na al’umma.

More from this stream

Recomended