Tarayyar Turai (EU) ta ba da tallafin karatu na mastas ga matasan Najeriya 135 a karkashin shirin Erasmus Mundus na 2023.
Ms Samuela Isopi, jakadiyar Tarayyar Turai a Najeriya ce ta bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja ranar Litinin.
“Wadanda za a ba da tallafin za su yi aiki don shirin mastas na watanni 12, wasu kuma na tsawon watanni 24 a kasashe uku daban-daban na EU, ciki har da Turkiyya, Birtaniya da Serbia.