Tankar dakon man Iran ta fashe a gabar tekun Saudiyya | BBC Hausa

Crude oil tanker, Amjad, which was one of two reported tankers that were damaged in mysterious

Hakkin mallakar hoto
AFP

Rahotanni daga Iran sun ce an samu fashewa a wata tankar dakon man Iran kusa da tashar ruwan Saudiyya a Jeddah.

Kafofin yada labaran Iran sun ce fashewar tankar ya haifar da tsiyayar mai a tekun Maliya.

Wata kafar talabijin din Iran Al Alam ta danganta fashewar da aikin ta’addanci.

Tankar mai suna Sinopa mallakin kamfanin man Iran ce.

Zuwa yanzu babu karin bayani kan ko akwai hasarar rayuka.

More from this stream

Recomended