Yan sanda sun kama basaraken gargajiya da ya yi wa yarinya yar shekaru 12 fyade

Rundunar yan sandan jihar Ondo ta ce jami’anta sun kama wani basaraken gargajiya a mai rike da sarautar  Baale a garin Laaagba dake karamar hukumar Ondo east kan zargin yin lalata da yarinya yar shekara 12.

Kafar yada labarai ta The Cable ta rawaito cewa basaraken gargajiyar mai suna, Adeniyi Ifedayo ya boye yarinyar a gidansa na tsawon makonni biyu yana cin zarafinta.

Yarinyar da ba a bayyana sunanta ba dake samun kulawar likitoci a wani asibiti dake Ondo da ba a bayyana ba ta ce wani mai  hayar babur ne ya hilace  ta zuwa gidan basaraken.

“Baale ya ajiye ni a gidansa na tsawon makonni biyu ya rika shayar da ni koko yana kuma lalata da ni a kullum,” ta ce.

” Iyaye na sun shiga damuwa da basu ganni ba shi ne  su ka yi yekuwar bacewa ta. Bayan sati biyu Baale  ya dauke ni a babur inda ya jefar da ni a  wani wuri dake Akure babban birnin jihar.”

T.Y Pickson  kwamanda shiyar Ondo na rundunar yan sandan Najeriya ya tabbatar da faruwar lamarin.

Pickson ya ce an tura batun ya zuwa hedkwatar rundunar dake Akure.

More from this stream

Recomended