Sokoto: An Kai Hari Ranar Sallah a Sabon Gari


A daidai lokacin da al’ummar Musulmi a fadin duniya ke shagulgulan sallah karama, al’ummomi a yankin karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto a arewacin Najeriya suka fuskanci wani tashin hankali.
A cewar wasu wadanda suka sheda harin mahara sun fito ranar sallah dauke da bindigogi, suka rinka harbin mutane.
Saboda tsananin harin, sai da aka dukkufa wajen tsintar gawarwaki na mutanen da ‘yan bindigan suka kashe.
Wani wanda ya sheda aukuwar lamarin, ya sheda wa Muryar Amurka cewa, “mutanen sun fito ne daga cikin wani daji wanda ke tsakanin Sabon Birni da garin Bature, inda suka hana kowa wucewa.
“Da muka lissafa gawarwakin mutanen da aka kashe, muna kan 14 a yanzu.”
Yayin da yake tsokaci kan harin, Kwamishinan tsaro a jihar ta Sokoto, Kanar Garba Moyi mai ritaya ya ce “maharan suna karanta yadda ake tsara wuraren da ake aika sojoji.”
“Ba zai yi wu a ajiye sojoji a kowanne kauye ba, suna lura da yadda sojojin ke tafiya daga kauye-kauye ne kafin su yanke shawarar inda za su kai hari.”
A cikin ‘yan kwannakin nan yadda ake kai hare-hare a yankin na kara kaimi.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...